Thursday, June 9, 2011

Yan siyasar Arewa.(Kodagai Akan Allon Wasan Dara Na Siyasar Najeriya.)


on Monday, May 17, 2010


Dara, wasa ne da ya ke dogaro da kaifin kwanya ba karfin kwanji ba. Akan allon wannan wasa, kodagan da ake amfani da su a matsayin mayaka suna da yawa. Aikin kowane kodago kuwa shi ne ya toshe duk wata kafa da zai sa a kusanci inda Sarauniya ta ke. Ran Sarauniya ne kadai ya ke da muhimmanci acikin wannan wasa, shi kadai ne abin karewa. Kodago kuwa mayaki ne saboda haka dole ya mutu wajen kare Sarauniya.

Nazariyyar shirya makarkashiya- Consipracy Theory- ba ta burge ni sosai. Ban kuma yi imani da cewa dukkan abinda ya ke faruwa a fagen siyasa makirci ne da ake kitsawa a tsakar dare ba saboda a aiwatar da shi idan gari ya waye. Sai dai wannan bai kore cewa da akwai 'yan siyasa masu kaifin kwakwalwa fiye da wasu ba. Wadanda su ke iya sarrafa 'yanuwansu 'yan siyasa kamar yadda marigayiya Ladi Kwali ta ke sarrafa laka saboda ta kera tukunya ko Randa ko kuma Kwatanniya.

"Yan siyasar arewa manyansu da kananansu kodagai ne da ake amfani da su a matsayin mayaka. Wace saruniya su ke karewa ? shi ne abinda ban sani ba. Sai dai ina da tabbacin cewa wannan Sarauniyar da su ke faduwa daya bayan wajen kare ta ba Daurama ba ce kuma ba Amina ba. Idan kuma na dubi taswirar siyasar Najeriya zan iya bugun kirji in ce Baba Aremu Obasanjo shi ne wanda ya ke kada su hagu da dama domin kare wannan Sarauniyar da na jahilta. Ba ni da shakkun cewa shi kwararren dan wasa ne da ya san abinda ya ke so ya ke kuma aiki tukuru domin cimma manufa.! Ba kuma laifinsa na ke gani ba saboda wannan baiwar da ya ke da ita.! Shekaru kusan goma a baya shugaban Kasar Uganda Yuweri Museveni ya fadi cewa:

"Ba ni ganin laifin turawa da su ka bautar da 'yan Afirka. Wadanda su ka tsaya aka kama su a matsayin bayi ne su ke da laifi."

Lokacin da Obasanjo ya tsaya a cikin birnin katsina ya rantse cewa idan marigayi Umar 'Yar'adua bai zama shugaban kasa ba shi ( Obasanjo) shege ne, mutanen da su ke zagaye da shi sun yi masa tafi. Babu wanda ya kalubalance shi sai lokacin da marigayin ya ke gargarar mutuwa.! A lokacin ne 'yan jarida su ka yi masa tambaya akan cewa zabar Umar da ya yi wani makirci ne da ya kulla domin ya san ba zai yi tsawon rai ba. Shi kuwa ya kare kansa da cewa liktoci sun fada masa cewa cutar da ya ke fama da ita ba za ta hana shi aiki ba.

Na tabbata mafi yawancin mutanen arewa idan ba dukkansu ba sun yi imani da cewa sanin lokacin mutuwar wani mahaluki gaibu ne da makullansa ke hannun Allah. Saboda haka batun Obasanjo ya dora Umar akan karagar mulki saboda idan ya rasu ya sake rike akalar siyasar kasa bai taso ba.! Saukin kan mutanen arewa  ( wanda ba abin yabo ba ne a siyasance) watakila kuma da karfin tasirin gubatacciyar fassarar addini sun rufe musu idanu akan su yi tunanin cewa dora 'Yar'adu'a akan karagar mulki yana da alaka da wasa na siyasa. Ko sun jahilta ko kuma suna sane amma sun rufe idanu cewa a karkashin wasa na siyasa wanda ya kashe abokin hamayyarsa zai iya shiga a yi masa salla jana'iza da shi kuma har ya zubar da hawaye. Tarihin siyasa cike ya ke da misalai irin wadandan da wadanda su ka fi su tayar da hankali.

Sun kuma sakankance cewa tunda dai doka ce ta jam'iyyar P.D.P cewa za a rika karba-karba tsakanin bangarorin kasa to ko bayan Umaru mulki zai ci gaba da zama a hannunsu. Obasanjo ya san cewa a lokacin da mutum ya ke da rauni zai iya mika wuya ga wata doka amma idan ya zama mai karfi ya sa kafa ya ta ke ta. A lokacin da jam'iyyar p.d.p ta yi waccan doka Obasanjo ba shi da iko da karfi saboda haka bai ki amincewa da ita ba. Yanzu da ya zama jan wuya a siyasar Najeriya, wanda kuma ya ke nadawa da saukewa babu abinda zai hana shi sa kafa ya take wannan doka.Wane dan arewa ne zai iya taka masa birki idan ya tsaya kai da fata sai Goodluck Jonathan ya tsaya takara? Ko kuma ya kawo wani wanda zai iya juya shi hagu da dama ya yi wasan kura da shi anan gaba?

Zabar Namadi Sambo a matsayin mataimakin shugaban kasa ya sake tabbatar da cewa wasan kura ake yi da 'yan siyasar arewa. Da kuma ace kungiyoyin arewa na sarakunan gargajiya da fararen hula da dukkan masu bakin fada a ji suna da 'yanci na tunani to da sun ki amincewa da wannan zaben.!. Idan ace wani gwamna ne daga wata jaha ta arewa aka baiwa wannan mukamin to da da sauki.Idan Obasanjo yana da hannu a cikin daukar wannan matakin to shakka babu ya yi wa mutanen arewa bugun mummuke- check mate - a makasa. Bani daga cikin masu cewa an zabe shi ne saboda zai yi saukin juyawa- duk da cewa ban kore hakan ba- amma na san sakamakon da zai biyo baya a kaduna yana da ban tsoro. Dauke Namadi daga kaduna tamkar motsa kodagon dara ne wanda zai jefa sarauniya cikin hatsari. Sarauniyar da na ke nufi anan wacce kuma na sani ita ce zaman lafiya na jahar kaduna.

Wadanda su ke kaduna suna da masaniya akan kwantaccen rikicin addini da kabilancin a cikin wannan jaha da ta ke a matsayin cibiyar arewa. Mutum zai iya bugun kirji ya ce dauke Namadi daga kaduna kada karaurawa ce mai hatsari akan abinda zai biyo baya. Abinda zai faru a lokacin zaben gwamnoni shi ne zai yanke hukunci.

Bani kare siyasar kabilanci da kowace kima, balle in ce dole sai dan arewa ya yi mulki amma ina cikin masu goyon bayan ayi aiki da doka. Idan doka ce rubutacciya ko kuma yarjejeniya koda kuwa ta baka ce akan cewa wannan lokaci ne na mulkin dan arewa to ya kamata 'yan arewan da su ke cikin p.d.p su kare hakkinsu. Ina kuma goyon bayansu akan haka amma ba saboda na yi imani da cewa za su tsinana wani abu ba.! Wanda zai ceto da kasa daga durkushewar da ta ke yi ne abin nema a daidai wannan lokacin mai hatsari ba dan wata kabila ko addini na musamman ba.

No comments:

Post a Comment